Bakonmu A Yau

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Amb Ibrahim Kazaure kan janye takunkumin ECOWAS ga kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso

    26/02/2024 Duración: 03min

    Kungiyar ECOWAS ta sanar da janye takunkumin karya tattalin arzikin da ta sanyawa kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, yayin da ta bukaci sojojin da suka yi juyin mulki a wadannan kasashe da su dawo teburin tattaunawa domin samo hanyar mayar da mulkin dimukiradiya a cikin su. Shugabannin ECOWAS sun ce an cire takunkumin ne saboda dalilan jinkai, kuma matakin ya kawo karshen hana zirga zirgar jiragen sama da bude asusun ajiyar wadannan kasashe guda 3. Dangane da tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Ibrahim Kazaure, masanin harkar diflomasiya.Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawar su ta gudana.....

  • Abdou Jibo kan takunkumin da ECOWAS ta sanyawa Jamhuriyar Nijar

    23/02/2024 Duración: 03min

    Kungiyar ‘Yan Nijar mazauna Cote d’Ivoire ta bukaci a cirewa Nijar takunkumai da aka kakaba mata sakamkon juyin mulki da sojoji suka yi, saboda halin kunci da hakan ya jefa su ciki. Shugaban kungiyar ta Ho consei de Nijar a Cote d’Ivoire Alhaji Abdou Jibo ya yi wannan kira, yayin zantawa ta musamman da sashin hausa na RFI a Abidjan.Amma ya fara yi wa Ahmad Abba bayani kan zamantakewarsu a kasar da ke mamba a ECOWAS.Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar

página 2 de 2